Surukar Ministan Yaɗa Labarai ta Rasu

A daren jiya Allah ya ɗauki ran Hajiya Hauwa, surukar Ministan Yaɗa Labarai Da Wayar Da Kai, Alhaji Mohammed Idris.

Mahaifiyar maiɗakin Ministan ta rasu ne sakamakon rashin lafiya, tana da shekaru 70 a duniya.

Mataimaki na Musamman ga Ministan, Hon. Saidu Enagi, ya bayyana cewa za a yi mata jana’iza a Babban Masallacin Ƙasa da ke Abuja a yau da ƙarfe 1:30 na rana.

Allah ya rahamshe ta, amin.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *