Gwamnati za ta sake zuba kuɗin da ake tarawa daga janye tallafin wutar lantarki wajen inganta wutar lantarki, kiwon lafiya, da ilimi, inji Ministan Yaɗa Labarai

Ministan Yaɗa Labarai Da Wayar Da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya ce sama da naira tiriliyan 1 da za a tara daga janye tallafin wutar lantarki za a sake zuba su ne wajen inganta wutar lantarki, kiwon lafiya, da ilimi ga ‘yan Nijeriya. Da yake jawabi a matsayin babban baƙo na shahararren shirin Rediyo Nijeriya…

Read More

Nijeriya ta yi Allah-wadai da harin da ake kai wa ‘yan jarida a Gaza, ta yi kira da a gaggauta tsagaita wuta a rikicin Isra’ila da Falasɗinu

Ministan Yaɗa Labarai Da Wayar Da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya yi Allah-wadai da harin da sojojin Isra’ila ke kai wa ‘yan jarida a rikicin da ke gudana a ƙasar Falasɗinu, yana mai jaddada cewa matakin na nuna take haƙƙin ‘yan jarida da kuma haƙƙin ɗan’adam. A cikin wata sanarwa da ya raba wa manema…

Read More