Shugaba Tinubu ya yi garambawul a tsarin Ministocinsa yayin da Wale Edun da Ahmed Dangiwa suka yi Murabus
Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya amince da yin ɗan takaitaccen garambawul a cikin majalisar ministocinsa, inda aka samu canjin wasu manyan ministoci biyu. Wata sanarwa da Sakataren Gwamnatin Tarayya, Sanata George Akume ya sanya wa hannu, ta bayyana cewa Ministan Kuɗi, Mista Wale Edun, da Ministan Gidaje da Raya Birane, Akitek Ahmed Musa Dangiwa,…
Dakarun Soji Sun Ragargaji Maboyar ’Yan Bindiga a Bauchi
Gwamnan Jihar Bauchi, Bala Mohammed, ya tabbatar da cewa dakarun sojin Najeriya sun yi nasarar fatattakar daruruwan ’yan bindiga tare da ruguza sansanoninsu a wasu samame na hadin gwiwa da suka gudanar a fadin jihar. Gwamna Mohammed ya bayyana hakan ne a ranar Litinin yayin da yake yi wa manema labarai bayani bayan kammala wani…
Shugaba Tinubu Ya Nada Dakta Fatima Sulaiman A Matsayin Sabuwar Shugaba A Hukumar NBMA
Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu ya amince da nadin Dakta Fatima Suleiman Zuntu a matsayin sabuwar Shugaba kuma Babban Jami’ar Gudanarwa (DG/CEO) ta Hukumar Kula da Kwayoyin Halittu ta Kasa (NBMA). Wannan nadin na kunshe ne a cikin wata sanarwa da fadar shugaban kasa ta fitar, inda aka bayyana cewa nadin nata zai kwashe tsawon…
TSARO: Goyon Bayan Gwamna Lawal Ga Sojoji Ba Kasafai Ake Samun Irin Sa Ba — Babban Hafsan Tsaro
Babban Hafsan Tsaron Nijeriya, Janar Olufemi Oluyede, ya yaba da irin gagarumin goyon bayan da Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ke bai wa rundunar Operation Fansan Yamma, yana mai cewa irin wannan tallafi ba kasafai ake ganin irinsa ba. Janar Oluyede ya bayyana hakan ne a yayin wata ziyarar aiki da ya kai Jihar Zamfara,…
Ma’aikatar Kuɗi Ta Karyata Zargin Ɓoye Kuɗaɗen Shiga Na Kasa
Ma’aikatar Kuɗi ta Tarayya ta mayar da martani kan wasu rahotannin kafafen yada labarai da suke ikirarin cewa ana karkatar da kuɗaɗen shigar ƙasa ko kuma ana yin “ɓoyayyen kashe-kashe.” Wadannan rahotanni sun biyo bayan fassarar da aka yi wa sabon rahoton Bankin Duniya (World Bank) kan tattalin arzikin Najeriya. Ma’aikatar ta bayyana cewa wadannan…
Shugaba Tinubu Ya Yi Ta’aziyyar Rasuwar Ibrahim Galadima
Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu ya nuna alhininsa kan rasuwar fitaccen mai kula da harkar wasanni kuma jagoran al’umma a Jihar Kano, Alhaji Ibrahim Galadima. Marigayi Galadima ya riga mu gidan gaskiya ne a ranar Asabar yana da shekaru 78 a duniya. Kafin rasuwarsa, Ibrahim Galadima ya rike mukamai daban-daban a matakin jiha da na…
NELFUND Ta Biya Wa Daliba 6,385 na Jami’ar Lafiya Kudin Makaranta Miliyan 795
Hukumar bayar da lamuni ga dalibai ta kasa (NELFUND), ta fitar da kudi har naira miliyan dari bakwai da casa’in da biyar da dubu dari bakwai da ashirin da tara da dari biyar (₦795,729,500) domin biyan kudin karatun dalibai dubu shida da dari uku da tamanin da biyar (6,385) na Jami’ar Gwamnatin Tarayya da ke…
Tallafin Noma: Gwamnatin Tarayya Za Ta Raba Dala Miliyan 500 Kai Tsaye Ga Manoma ‘Na Gaskiya’
Gwamnatin Tarayya ta bayyana aniyar ta na ganin cewa tallafin dala miliyan 500 da Bankin Duniya ya amince da shi, ya isa hannun manoma na hakika a fadin kasar nan, maimakon karkata shi ga akwakun ‘yan siyasa. Shugaban Hukumar Ba da Tallafin Kuɗaɗen Haɗin Gwiwa na Ƙasa (NFC), Emmanuel Atama, shi ne ya tabbatar da…
CBN ya ƙaddamar da sabon gejin ma’aunin ƙarfafa tsarin hadahadar kuɗi
Ashafa Murnai Barkiya Kasuwar hadahadar kuɗi ta Nijeriya ta samu tagomashin babban sauyi, yayin da Babban Bankin Nijeriya (CBN), tare da haɗin gwiwar Ƙungiya Masu Cibiyoyin Hadahadar Kuɗi, wato ‘Financial Markets Dealers Association’ (FMDA), suka ƙaddamar da sabon tsarin shata ƙima da ma’aunin ribar rance ko lamuni, mai suna ‘Nigerian Overnight Financing Rate’ (NOFR). An…
Shugaba Tinubu Ya Sa Hannu Kan Dokar Kasafin Kuɗin 2026 Da Na Tsawaita Lokacin Kasafin 2025
Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya amince da kasafin kuɗin shekarar 2026, wanda jimillar kuɗaɗen da za a kashe a cikinsa suka kai naira triliyan 68.32. Haka kuma, Shugaban ya sanya hannu kan dokar tsawaita lokacin aiwatar da ayyukan babban birnin na kasafin kuɗin 2025 daga ranar 31 ga Maris, 2026, zuwa 30 ga watan…
