GABA DAI GABA DAI CBN: Ma’aunin yawan hadahadar masana’antu, kamfanoni da kasuwanci (PMI) ya kai maki 55.7 a watan Janairu
Ashafa Murnai Barkiya Bayanan da Babban Bankin Njeriya (CBN) ya fitar cikin wannan mako sun nuna cewa ma’aunin ƙarfin harkokin tattalin arzikin ƙasar sun ci gaba da nuna ƙarfi sosai a watan Janairu 2026, inda Ma’aunin hadahadar cinikayya a masana’antu, kamfanoni da kasuwanci, wato (Purchasing Managers’ Index – PMI) na CBN ya ƙaru zuwa maki…
Sauye-sauyen tattalin arzikin Tinubu suna daidaita Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai
Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya ce sauye-sauyen tattalin arziki da Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu yake aiwatarwa suna daidaita tattalin arzikin Nijeriya, maido da amincewar jama’a, tare da sanya ƙasar nan kan tafarkin cigaba mai ɗorewa bayan shekaru da dama na rashin tabbas. Ministan ya bayyana hakan ne yayin…
“Mulkin Tinubu zai zama kyakkyawan fata ga ‘yan Najeriya” — Limamin Masallacin Ƙasa
Limamin da ya jagoranci ɗaurin auren ’ya’yan Ƙaramin Ministan Tsaro, Alhaji Mohammed Bello Matawalle, Farfesa Luqman Zakariyah, ya yi wa Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu addu’a, yana mai cewa mulkinsa zai dawo da kyakkyawan fata a cikin al’umma. Farfesa Zakariyah ya yi addu’ar ne a ranar Juma’a a Masallacin Ƙasa da ke Abuja, yayin da…
Shugaba Tinubu ya gana da Gwamnan Kwara
Shugaban Ƙasa Bola Tinubu ya karɓi bayanai a yau Alhamis daga Gwamna AbdulRahman AbdulRazaq game da harin ’yan ta’adda da aka kai a Worro, ƙaramar hukumar Kaiama ta Jihar Kwara.
An yi wa masu POS rijista ne don inganta tsaro, cewar Ministan Yaɗa labarai
“Ɗaya daga cikin dalilan da ya sa gwamnatin tarayya ta yi rajistar masu POS shi ne ƙara inganta tsaro ga ’yan ƙasa a faɗin ƙasar nan.Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Mohammed Idris, ya yi wannan jawabi ne yayin da ya karbi bakuncin Shugaban Hukumar Rijistar Kamfanoni ta Najeriya (CAC), Hussaini Ishak Magaji, a…
Hukumar CAC ta zama ginshiƙin amintaccen tattalin arzikin Nijeriya, inji Idris
Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya sake jaddada ƙudirin Gwamnatin Tarayya na tabbatar da gaskiya, aiwatar da sauye-sauye a hukumomi, da sauƙaƙe harkokin kasuwanci, inda ya bayyana cewa haɗin gwiwar hukumomi shi ne ginshiƙi wajen cimma manufofin Shirin Sabunta Fata Nagari na Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu. Idris ya bayyana…
Gwamnatin Tarayya ta kaddamar da shirin horar da ’yan Najeriya miliyan 10 kan hada-hadar kudi
Gwamnatin Tarayyar Najeriya ta kaddamar da shirin horas da ’yan kasa miliyan 10 kyauta kan ilimin hada-hadar kudi da shigar kudi cikin tsari, inda ta ce matasa da mata ne ginshikin cin gajiyar yawan al’ummar kasar. Mataimakin Shugaban Kasa, Sanata Kashim Shettima, ya bayyana hakan a fadar shugaban kasa da ke Abuja, yayin da yake…
RAHOTON MUSAMMAN: Yadda Asusun Kuɗaɗen Waje Na Nijeriya Zai Cika Maƙil, Bayan CBN Ya Yi Wa Naira Allurar Ƙarin Ƙarfin Wujijjiga Dala A Tsakiyar Kasuwa
RAHOTON MUSAMMAN Daga Ashafa Murnai Barkiya Tun sabuwar shekarar nan ta 2026 ba ta yi nisa ba, alamomi na ci gaba da nuna cewa, tsare-tsaren ƙarfafa hadahadar kuɗaɗe, bunƙasa tattalin arziki da sauƙaƙa farashi wanda Babban Bankin Nijeriya (CBN) ya bijiro da shi zai samar da gagarimin ci gaba. Hakan na zuwa ne daidai lokacin…
Jaridar THE SUN Ta Karrama Gwamnan Zamfara Da Lambar Yabo Ta ‘Gwamnan Shekarar 2025’
Gwaman Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya samu wata babbar karramawa bayan da jaridar The Sun ta ba shi lambar yabo ta “Gwamnan Shekarar 2025”, sakamakon abin da aka bayyana a matsayin gagarumar nasara da gwamnatinsa ta samu a fannin shugabanci nagari. An miƙa lambar yabon ne a wani gagarumin biki na Sun Awards da aka…
Gwamna Lawal Ya Ƙaddamar Da Manyan Ayyuka A Tsafe Domin Farfaɗo Da Ci Gaban Al’umma
Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya sake jaddada cewa duk wani ci gaba da gwamnati za ta aiwatar dole ne ya kasance mai anfani kai tsaye ga rayuwar al’umma, tare da samar da sauyi mai ma’ana. Gwamnan ya bayyana hakan ne a ranar Juma’a yayin da ya ƙaddamar da muhimman ayyuka biyar a Ƙaramar Hukumar…
