An Sake Karrama Gwamna Dauda Lawal Da Lambar Yabo Kan Mulki Na Adalci A Zamfara
Gwamnan jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya karɓi lambar yabo ta ƙwarewa daga Hukumar Daidaita Shirye-shiryen Tallafin Jinƙai ta Ƙasa (NASSCO) bisa irin ƙoƙarin gwamnatin sa wajen tabbatar da mulki na adalci da kuma aiwatar da shirye-shiryen kare marasa ƙarfi a jihar Zamfara. An bai wa gwamnan lambar yabon ne yayin taron tattaunawa da masu ruwa…
Shugaba Tinubu Ya Shiga Takarar Wa’adi Na Biyu Yayin Da Mataimakinsa Shettima Ya Mika Fom ga APC
A yau Alhamis 7 ga watan Mayu ne, Mataimakin Shugaban Najeriya Kashim Shettima ya kaddamar da neman takarar Shugaba Bola Ahmed Tinubu a hukumance ga uwar jam’iyyar APC ta kasa. A wani gagarumin taro da aka gudanar a dakin taro na Bola Ahmed Tinubu International Conference Centre Mataimakin ya jagoranci mambobin jam’iyyar da suka hada…
NAZARI: Ƙaƙudubar kasa biyan tulin bashin da manyan bankuna suka bayar laifin daraktoci da manyan masu hannayen jarin su ne, ba laifin CBN ba
Daga Ashafa Murnai Barkiya Yayin da ake fama da gagarimar matsalar yawan maƙudan kuɗaɗen da bankuna suka bayar bashi, kuma biyan bashin ya gagara, akwai masu ɗora laifin kan Babban Bankin Nijeriya (CBN), a matsayin sa na mai kula da kuma sa-ido kan dukkan bankunan Nijeriya. To sai dai kuma idan aka yi la’akari da…
BABBAN LABARI: Tsauraran matakai da ƙa’idojin da CBN ya gindaya, dangane da bashin naira tiriliyan 2.9 da kamfanin Nestoil ya kasa biyan wasu bankunan Nijeriya
Tsauraran matakai da ƙa’idojin da CBN ya gindaya, dangane da bashin naira tiriliyan 2.9 da kamfanin Nestoil ya kasa biyan wasu bankunan Nijeriya *Yadda katutun bashin ya jawo jinkirin raba ribar ƙarshen shekarar 2025 a wasu manyan bankuna Daga Ashafa Murnai Barkiya Kamfanin ɗanyen mai na Nestoil mallakar attajiri Ernest Obiejesi ya jefa wasu manya…
Shugaba Tinubu ya gana da manyan masu zuba jari na duniya a birnin Paris
Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya gana da manyan masu zuba jari na duniya a birnin Paris na ƙasar Faransa, inda ya jaddada aniyar gwamnatin sa na tabbatar da gaskiya, adalci, da kuma kiyaye ka’idojin kashe kuɗi. Shugaban ya kuma bayyana dalilan da suka sa aka aiwatar da garambawul ga tattalin arziki cikin gaggawa. A yayin…
Shugaba Tinubu Ya Taya Murtala Garo Murnar Zama Mataimakin Gwamnan Kano
Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya taya Alhaji Murtala Sule Garo murnar rantsar da shi a matsayin sabon Mataimakin Gwamnan Jihar Kano, wanda Gwamna Abba Kabir Yusuf ya kaddamar a ranar Talata. Gwamna Abba ya nada Murtala Garo ne domin cike gurbin da Comrade Aminu Abdulsalam ya bari, bayan murabus din da ya yi biyo bayan…
Yadda ƙarfin laƙani da dafa’in CBN ke hana girgizar tattalin arzikin duniya yi wa Nijeriya barazana
Daga Ashafa Murnai Barkiya Manyan sauye-sauyen da Babban Bankin Nijeriya (CBN) ya aiwatar, sun zama ƙaƙƙarfar kariya ga girgizar tattalin arzikin duniya, suna kuma taimakawa wajen tabbatar da amincewar masu zuba jari da kuma ƙara hasashen bunƙasar tattalin arziki. Sauye-sauyen da CBN ƙarƙashin jagorancin Olayemi Cardoso ya gabatar sun shirya tattalin arzikin ƙasar don jure…
Ranar ’Yancin ’Yan Jarida ta Duniya: Gwamnatin Nijeriya ta nemi haɗin gwiwa don yaƙi da yaɗa labaran ƙarya
Gwamnatin Tarayyar Nijeriya ta buƙaci a ƙara haɗin gwiwa tsakanin kafafen yaɗa labarai, hukumomin gwamnati da sauran masu ruwa da tsaki domin magance barazanar yaɗa labaran ƙarya. Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, shi ne ya bayyana hakan a ranar Litinin a Abuja yayin bikin Ranar ’Yancin ’Yan Jarida ta Duniya…
Shirin Ɗaƙile Harƙalla: Yadda CBN ke amfani da Sashen Bankaɗo Kuɗaɗen da ake Karkatarwa (SCUML)
Ashafa Murnai Barkiya Cikin makon jiya ne Babban Bankin Nijeriya (CBN) ya fitar da wani faifan bidiyo mai ɗauke da bayanan sigogi da illolin laifukan karkatar da kuɗaɗe ga ƙasar nan da kuma tattalin arzikin ta. Bidiyon mai ɗauke da bayanan mintina kusan shida, ya kuma ƙunshi irin hukuncin da doka ta tanadar wa masu…
TARON APC A ZAMFARA: Gwamna Lawal Ya Tabbatar Da Cewa Ƙarfin Gwamnati Na Rataye Ne Da Kyawawan Tsare-tsaren Jam’iyya
Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya jaddada cewa nasara da ɗorewar kowace gwamnati na da alaƙa kai tsaye da ƙarfinta a fagen siyasa, musamman yadda jam’iyyarta ke da tsari mai ƙarfi da haɗin kai. Gwamnan ya bayyana hakan ne a ranar Asabar yayin da ya halarci taron zaɓen shugabannin jam’iyyar APC na Jihar Zamfara, wanda…
