Gwamnan CBN ya jaddada muhimmancin ƙarfafa cibiyoyi da gyaran jarin bankuna domin bunƙasar tattalin arziki mai ɗorewa
Ashafa Murnai Barkiya Gwamnan Babban Bankin Nijeriya (CBN), Mista Olayemi Cardoso, ya jaddada buƙatar gina cibiyoyi masu ƙarfi da kuma kyawawan ginshiƙan harkokin kuɗi domin tabbatar da bunƙasar tattalin arziki mai ɗorewa a Nijeriya. Cardoso ya yi wannan kira ne yayin da yake gabatar da lacca ta musamman ga tsofaffin ɗalibai a bikin Founders’ Day…
Shugaba Tinubu Ya Nemi Amincewar Majalisa Kan Nadin Lamido Yuguda a Matsayin Mataimakin Gwamnan CBN
Fadar Shugaban Ƙasa ta sanar da cewa Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya amince da naɗin Lamido Abubakar Yuguda a matsayin Mataimakin Gwamnan Babban Bankin Najeriya (CBN), sai dai naɗin zai fara ne bayan Majalisar Dattawa ta tabbatar da shi. Sanarwar ta fito ne daga Mai Bai wa Shugaban Ƙasa Shawara kan Harkokin Yaɗa Labarai da…
Gwamnatin Tarayya Na Shirin Faɗaɗa Amfani Da Gas Da Motocin Lantarki Don Rage Tsadar Sufuri — PCNGI
Shugaban Hukumar Presidential Compressed Natural Gas Initiative (PCNGi), Ismaeel Ahmad, ya ce gwamnati na ƙara ƙaimi wajen faɗaɗa amfani da gas da motoci masu amfani da lantarki domin rage tsadar sufuri a Najeriya. Ismaeel ya bayyana haka ne bayan ganawarsa da Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu, inda suka tattauna kan hauhawar farashin fetur da rikicin…
Gwamnati: Haɗaɗɗiyar hanyar yaɗa labarai za ta ƙarfafa daidaiton tsaron ƙasa, ta yaba da gyaran iyakoki ta amfani da fasaha
Hagu zuwa dama: Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris; Ministan Harkokin Cikin Gida, Dakta Olubunmi Tunji-Ojo; da Babbar Sakatariyar Ma’aikatar Harkokin Cikin Gida ta Tarayya, Dakta Magdalene Ajani, a lokacin ziyarar aiki da Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai ya kai wa Ma’aikatar Harkokin Cikin Gida a ranar Talata, 10…
Tinubu Da Shettima Sun Yi Buɗa-Baki Da Sarakuna Da Malaman Addini A Villa
Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu tare da Mataimakinsa Kashim Shettima sun yi buɗa-bakin azumin watan Ramadan tare da sarakuna da kuma shugabannin addinai a Banquet Hall na Fadar Shugaban Ƙasa da ke Villa, Abuja. Taron buɗa-bakin wanda ya gudana a ranar Litinin ya haɗa manyan shugabannin gargajiya da malaman addini daga sassa daban-daban na ƙasar,…
Dalilin Da Ya Sa Na Sauya Sheƙa Zuwa APC – Gwamna Dauda Lawal
Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayyana cewa rikicin cikin gida da kuma taƙaddamar shari’a da ke addabar Jam’iyyar PDP su ne manyan dalilan da suka sa ya yanke shawarar sauya sheƙa zuwa Jam’iyyar APC. Mataimakin Gwamnan Jihar Zamfara, Malam Mani Mummuni, ne ya sanar da sauyin sheƙar a hukumance a ranar Litinin, bayan wani…
Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal Ya Sauya Sheƙa Zuwa APC
Gwamnan jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya sanar da ficewarsa daga jam’iyyar PDP tare da komawa jam’iyyar mai mulki ta APC. Cikin wata Sanarwar da ta fito a ranar Litinin cikin mai ɗauke da sa mai taimaka wa gwamnan kan harkokin yaɗa labarai, Nuhu Anka, ta bayyana cewa matakin ya biyo bayan dogon tuntuba da shugabannin…
RAHOTON MUSAMMAN: CBN ya umurci bankuna su yi gwajin ƙarfin jure matsin tattalin arziki
Ashafa Murnai Barkiya Yayin da saura makonni uku wa’adin ƙarfafa jarin bankuna da Babban Bankin Nijeriya (CBN) ya gindaya su cika, yanzu kuma CBN ya umarci dukkan bankunan kasuwanci su yi gwajin ƙarfin juriyar matsin tattalin arziki, wato ‘stress test’. Wannan umarni ya zo ne yayin da yake ci gaba da sa-ido kan tsarin bankunan…
Tinubu ga sojojin Nijeriya: Za mu yi galaba, sadaukarwar ku ba za ta tafi a banza ba
Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu a ranar Juma’a ya tabbatar wa ’yan Nijeriya da Sojojin Nijeriya cewa ƙasar nan za ta yi nasara a ƙarshe a kan dukkan nau’o’in rashin tsaro, yana mai jaddada cewa sadaukarwar jaruman sojojin ƙasar nan ba za ta tafi a banza ba. Mai Bai wa Shugaban Ƙasa Shawara na Musamman…
Bankuna 30 Suka Cika Sabbin Ƙa’idojin Ƙarfafa Jari -CBN
Ashafa Murnai Barkiya Babban Bankin Nijeriya (CBN) ya bayyana takamaiman yawan bankuna 30 cewa sun rigaya sun cika sabbin ƙa’idojin mafi ƙarancin jarin da ake buƙata bisa irin lasisin da kowannen su yake da shi.CBN ya ce a ranar 6 ga Maris, 2026 aka samu yawan wannan adadin bankunan. CBN ya kuma bayyana cewa gaba…
