Gwamnatin Tarayya ta kaddamar da shirin horar da ’yan Najeriya miliyan 10 kan hada-hadar kudi
Gwamnatin Tarayyar Najeriya ta kaddamar da shirin horas da ’yan kasa miliyan 10 kyauta kan ilimin hada-hadar kudi da shigar kudi cikin tsari, inda ta ce matasa da mata ne ginshikin cin gajiyar yawan al’ummar kasar. Mataimakin Shugaban Kasa, Sanata Kashim Shettima, ya bayyana hakan a fadar shugaban kasa da ke Abuja, yayin da yake…
RAHOTON MUSAMMAN: Yadda Asusun Kuɗaɗen Waje Na Nijeriya Zai Cika Maƙil, Bayan CBN Ya Yi Wa Naira Allurar Ƙarin Ƙarfin Wujijjiga Dala A Tsakiyar Kasuwa
RAHOTON MUSAMMAN Daga Ashafa Murnai Barkiya Tun sabuwar shekarar nan ta 2026 ba ta yi nisa ba, alamomi na ci gaba da nuna cewa, tsare-tsaren ƙarfafa hadahadar kuɗaɗe, bunƙasa tattalin arziki da sauƙaƙa farashi wanda Babban Bankin Nijeriya (CBN) ya bijiro da shi zai samar da gagarimin ci gaba. Hakan na zuwa ne daidai lokacin…
Jaridar THE SUN Ta Karrama Gwamnan Zamfara Da Lambar Yabo Ta ‘Gwamnan Shekarar 2025’
Gwaman Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya samu wata babbar karramawa bayan da jaridar The Sun ta ba shi lambar yabo ta “Gwamnan Shekarar 2025”, sakamakon abin da aka bayyana a matsayin gagarumar nasara da gwamnatinsa ta samu a fannin shugabanci nagari. An miƙa lambar yabon ne a wani gagarumin biki na Sun Awards da aka…
Gwamna Lawal Ya Ƙaddamar Da Manyan Ayyuka A Tsafe Domin Farfaɗo Da Ci Gaban Al’umma
Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya sake jaddada cewa duk wani ci gaba da gwamnati za ta aiwatar dole ne ya kasance mai anfani kai tsaye ga rayuwar al’umma, tare da samar da sauyi mai ma’ana. Gwamnan ya bayyana hakan ne a ranar Juma’a yayin da ya ƙaddamar da muhimman ayyuka biyar a Ƙaramar Hukumar…
Jihohi 27 ne suka kuɓuta daga durƙushewar tattalin arziƙi sakamakon sauye-sauyen Gwamnatin Shugaba Tinubu — Mohammed Idris
Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kan jama’a, Alhaji Mohammed Idris, ya ce sauye-sauyen da Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya aiwatar sun ceci aƙalla jihohi 27 a Najeriya daga faɗawa cikin mummunan durƙushewar tattalin arziƙi. Ministan ya bayyana hakan ne a ranar Asabar yayin da yake gabatar da lacca a bikin yaye ɗalibai karo na…
Gwamnatin Tarayya na tallafa wa matasa a fagen ilimi da ƙwarewar komfuta domin ƙarfafa Nijeriya a duniya – Idris
Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya shawarci matasan Nijeriya da su yi amfani da damarmakin da gyare-gyaren ƙasa da ake aiwatarwa suke samarwa, yana mai bayyana su a matsayin muhimman hanyoyi na cigaban kai da gina ƙasa. Ministan ya bayyana haka ne yayin gabatar da Laccar Kammala Karatu ta shekarar…
Sojojin Najeriya sun yi nasarar kashe babban kwamandan ISWAP a Arewa maso Gabas
Sojojin Operation Hadin Kai sun sake samun gagarumar nasara a yaƙin da suke yi da ’yan ta’adda a Arewa maso Gabas, inda suka kashe wani babban kwamandan ISWAP mai suna Julaibib a yankin Kimba, cikin Karamar Hukumar Damboa ta Jihar Borno. Bayanai sun nuna cewa marigayin na daga cikin manyan jagororin da ke ta’addanci a…
Haƙuri da addinin juna shi ne jigon zaman lafiya da haɗin kan Nijeriya – Tinubu
Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya yi kira ga ’yan Nijeriya da su rungumi haɗin kai, haƙurin addini, da zaman lafiya, yana mai bayyana su a matsayin muhimman ginshiƙan tsaron ƙasa da ci gaba mai ɗorewa. Shugaban Ƙasar ya yi kiran ne a wurin taron ƙasa da ƙasa karo na huɗu na Cibiyar Wayewar Musulunci…
Miƙa Saƙon Gwamnati Iri Ɗaya Shi Ne Ginshiƙin Dawo Da Amincewar Jama’a — Minista
Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya jaddada buƙatar gwamnati ta a riƙa yin saƙo iri ɗaya, daidaitacce, kuma wanda aka tsara shi da nufin samun amincewar jama’a, a matsayin muhimmin ginshiƙi na aiwatar da manufofin Shirin Sabunta Fata na Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu. Ministan ya yi wannan kiran ne…
Mataimakin Shugaban Ƙasa ya Kaddamar da Shirin Sake Tsugunar da Al’ummar Tudun Biri a Kaduna
Mataimakin Shugaban Ƙasa, Sanata Kashim Shettima, ya kaddamar da Shirin Sake Tsugunar da Al’ummar Tudun Biri da ke Karamar Hukumar Igabi a Jihar Kaduna, biyo bayan alkawarin da Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya yi na sake gina yankin bayan hatsarin jefa bam na soji bisa kure da ya faru kimanin shekaru biyu da suka gabata….
