2027: Tinubu ya zama ɗan takarar APC tare da alƙawarin ƙarfafa sauye-sauye
Shugaban Ƙasa Bola Tinubu a ranar Lahadi ya karɓi tikitin takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar APC domin zaɓen shekarar 2027, inda ya yi alƙawarin ƙarfafa sauye-sauyen da ake yi da kuma zurfafa cigaban ƙasa. Tinubu ya bayyana hakan ne a Abuja yayin da yake gabatar da jawabin karɓar takara bayan ya zama ɗan takarar shugaban…
Yaren Hausa Da Yarbanci Na Cikin Harsuna 35 Da Za A Fassara Huɗubar Arfa Kai Tsaye A Bana
Daga Aliyu Samba Mahukuntan Ƙasar Saudiyya sun sanar da cewa za a fassara huɗubar ranar Arfa ta Hajjin shekarar 2026 zuwa harsuna 35 na duniya, ciki har da Hausa da Yarbanci daga Najeriya, domin bai wa miliyoyin Musulmai damar sauraron saƙonnin huɗubar cikin yarukan da suka fi fahimta. Shirin, wanda Hukumar Kula da Harkokin Addini…
Shugaba Tinubu Ya Bayyana Zaɓen Fidda Gwanin APC A Matsayin Ƙwarin Gwiwar Ɗorewar Dimokuraɗiyya
Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, ya bayyana zaɓen fidda gwanin jam’iyyar APC da aka gudanar a faɗin ƙasar a matsayin wata alama ta ƙarfi da bunƙasar dimokuraɗiyyar cikin gida a jam’iyyar mai mulki. Tinubu ya bayyana haka ne bayan ya kaɗa ƙuri’arsa a zaɓen fidda gwani na jam’iyyar da aka gudanar a mazabar Ikoyi-Obalende Ward…
Gwamnatin Tinubu Ta Tabbatar Da Kammala Jigilar Alhazan Najeriya Sama Da 40,000 Zuwa Saudiyya Cikin Nasara
Daga Aliyu Samba An samu wani babban gagarumin nasara a harkokin aikin Hajjin shekarar 2026 yayin da Hukumar Alhazai ta Kasa (NAHCON) ta kammala jigilar alhazan Najeriya zuwa Ƙasar Saudiyya cikin nasara, inda aka yi jigilar alhazai sama da 40,000 cikin kwanaki 18 kacal. Wannan nasara ta sake tabbatar da irin kulawa da muhimmancin da…
Gwamna Dauda Lawal Ya Zama Ɗan Takarar APC A Zamfara, Ya Yi Alƙawarin Ƙara Ayyukan Ci Gaba
Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya yi alƙawarin ci gaba da ƙara ayyukan raya ƙasa domin inganta rayuwar al’ummar jihar. A ranar Alhamis ne gwamnan ya zama ɗan takarar jam’iyyar APC domin zaɓen gwamnan jihar Zamfara na shekarar 2027. Wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sulaiman Bala Idris, ya fitar ta bayyana cewa…
Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaryata Raɗe-Raɗin Canza Sunan Najeriya Da Soke Shari’a A Arewa
Fadar Shugaban Kasa ta karyata wani rahoto da ke yawo a kafafen sada zumunta da ke ikirarin cewa Shugaba Bola Ahmed Tinubu na shirin sauya sunan Najeriya zuwa “United States of Nigeria” tare da soke dokar Shari’a a Arewacin kasar. A cikin wata sanarwa da Mai Bai Wa Shugaban Kasa Shawara Kan Harkokin Yada Labarai…
Najeriya da Poland Za Su Haɗa Kai Kan Tsaro da Bunƙasa Tattalin Arziƙi
Gwamnatin Tarayya ta bayyana shirinta na yin aiki kafada da kafada da ƙasar Poland wajen inganta harkokin tsaron cikin gida da bunƙasa tattalin arziki. Ministan Harkokin Cikin Gida, Dakta Olubunmi Tunji-Ojo, ne ya bayyana hakan yayin da ya karɓi Mataimakin Firaministan Poland, Krzysztof Gawkowski, a ofishinsa da ke Abuja ranar Alhamis. Tunji-Ojo ya ce Najeriya…
Shugaba Tinubu ya naɗa Farfesa Segun Aina Magatakardan JAMB
Shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya naɗa Farfesa Segun Aina a matsayin sabon Magatakardar Hukumar Shirya Jarabawar Shiga Manyan Makarantu ta Ƙasa (JAMB), inda zai gaji Farfesa Is-haq Oloyede, wanda wa’adinsa na biyu zai ƙare a ranar 31 ga Yuli, 2026. Hakan na ƙunshe a wata sanarwa da Bayo Onanuga mai bai wa shugaban ƙasa…
Taron Kwamitin Manufofin Kuɗi na 305: Masana da masu ƙananan sana’o’i sun yaba da barin kuɗin ruwa da CBN ya yi a kashi 26.5%
Daga Ashafa Murnai Barkiya Masana tattalin arziki, manazarta harkokin kuɗi da kuma masu ƙananan sana’o’i sun yaba da matakin da Babban Bankin Nijeriya (CBN) ya ɗauka na barin kuɗin ruwa na Manufofin Kuɗi (MPR) a matakin kashi 26.5%. Waɗanda aka sanya da su domin jin ra’ayin su dangane da adadin kuɗin ladar karɓar lamiɗo a…
Gwamnatin Zamfara Ta Yi Wa Mutane 6,842 Magani Kyauta A Kashi 17 Na Shirin Tallafin Lafiya
Gwamnatin Jihar Zamfara ta bayyana cewa, ta gudanar da aikin kula da marasa lafiya 6,842 ta hanyar babban shirin tallafin lafiya kyauta da aka tanada domin yi wa al’umma tiyata da sauran kulawar lafiya ba tare da biyan kuɗi ba. A cikin wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan jihar, Sulaiman Bala Idris, ya…
