Cardoso ya ƙaddamar da Ƙungiyar Jakadun Naira na CBN
Daga Ashafa Murnai Barkiya Gwamnan Babban Bankin Njeriya (CBN), Olayemi Cardoso, ya ƙaddamar da Ƙungiyar Jakadun Naira na CBN, wani shiri da aka samar domin wayar da kan al’umma, musamman matasa kan muhimmancin kare daraja da martabar takardun Naira da kuma kula da yadda ake amfani da ita. Da yake jawabi a wajen ƙaddamar da…
Tattalin arziƙin Nijeriya ya inganta fiye da na 2023 – Jakada Omokri
Tsohon mai ba Shugaban Ƙasa shawara kuma Jakaden Nijeriya da aka naɗa zuwa ƙasar Meziko, Reno Omokri, ya kare ayyukan gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu, inda ya bayyana cewa tattalin arzikin Nijeriya ya fi ƙarfi a yanzu idan aka kwatanta shi da lokacin da Shugaban ya hau mulki a shekarar 2023. A cikin wata sanarwa…
Kashim ya Halarci Bikin Cika Shekaru 70 na Sarkin Lafia, Ya Ƙaddamar da Sabbin Hanyoyi
Mataimakin Shugaban Ƙasa, Sanata Kashim Shettima, ya halarci bikin cika shekaru 70 da kuma bikin bankwana da aiki na Sarkin Lafia, Mai Martaba Justice Sidi Bage Muhammad (mai ritaya), wanda aka gudanar a birnin Lafia na Jihar Nasarawa. A jawabinsa, Sanata Shettima ya bayyana cewa samun zaman lafiya mai ɗorewa da ci gaban Najeriya na…
Jami’an Tsaro Sun Kama Makamai Da Ake Shirin Kai Wa ’Yan Ta’adda A Kogi
Haɗin gwiwar jami’an tsaro ƙarƙashin jagorancin Gwamnatin Tarayya ya yi nasarar kama makamai da alburusai da ake zargin an shirya kai wa ’yan ta’adda a Jihar Kogi. A wata sanarwa da Kwamishinan Yaɗa Labarai na Jihar Kogi, Kingsley Femi Fanwo, ya fitar, ya ce nasarar ta samu ne sakamakon haɗin gwiwa tsakanin jami’an tsaro na…
Duk Mai Yin Sulhu Da ‘Yan Ta’adda, Ba Da Yawun Gwamnatin Mu Ba Ne, In Ji Gwamnan Zamfara
Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya sake jaddada matsayar gwamnatin sa na ƙin shiga tattaunawa ko ƙulla yarjejeniyar sulhu da ’yan bindiga, yana mai cewa gwamnatin jihar ba za ta amince da zaman sulhu da ƙungiyoyin masu aikata laifuka ba. Gwamnan ya bayyana hakan ne a wata hira da ya yi da Sashen Hausa na…
Saudiyya ta ƙaddamar da rabon tallafin abinci na bana
Ofishin Jakadancin Masarautar Saudiyya da ke Abuja, ta hannun Cibiyar Agaji da Tallafin Jinƙai ta Sarki Salman (KSrelief), tare da haɗin gwiwar Hukumar Ba da Agajin Gaggawa ta Ƙasa (NEMA), sun ƙaddamar da Shirin Tallafin Abinci na shekarar 2026 domin tallafa wa al’ummomin da suka fuskanci matsalolin ƙaura, rashin tsaro da sauran ƙalubalen jinƙai a…
Kashim Ya Halarci Addu’ar Shekara-shekara Domin karrama Mahaifiyar shugaba Tinubu a Abuja
A yau a Masallacin Ƙasa da ke Abuja, Mataimakin Shugaban Ƙasa, Sanata Kashim Shettima, ya halarci taron addu’ar shekara-shekara da aka gudanar domin karrama marigayiya Alhaja Abibatu Mogaji, mahaifiyar Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu. A jawabinsa, Sanata Shettima ya bayyana marigayiyar a matsayin mace mai tarbiyya da tasiri, wacce ta bar gagarumin tarihi da zai…
Rahoton CBN: Bayanan yadda ‘yan damfara suka kwashe naira biliyan 134 daga asusun bankuna da na kwastomomi tsakanin 2020 zuwa 2025
Ashafa Murnai Barkiya Rahoton baya-bayan nan da Babban Bankin Nijeriya (CBN) ya fitar, ya nuna cewa bankuna da kwastomomin su sun yi asarar jimillar Naira biliyan 134.48 sakamakon damfara a tsakanin shekarar 2020 zuwa 2025. Rahoton ya bayyana cewa an yi yunƙurin damfara da ya kai Naira biliyan 187.79, amma dai takamaiman adadin da ya…
YAƘI DA TA’ADDANCI: Gwamnan Zamfara Ya Jinjina Wa Jami’an Tsaro Bisa Ƙwato Ɗarurruwan Shanu
Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya yaba wa jami’an tsaro bisa ƙoƙarin da suke yi da jajircewarsu wajen yaƙi da ayyukan ’yan bindiga a jihar. Yabon na gwamnan ya biyo bayan nasarar da Sashen Daƙile Ayyukan Ta’addanci da Rikice-rikice, wato Violence Crime Response Unit – VCRU, na Rundunar ’Yan Sandan Jihar Zamfara ya samu na…
Gwamnatin Tarayya ta Raba Buhunan Taki 100,800 ga Manoma 25,200 a Arewa maso Yamma
Gwamnatin Tarayya ta ƙarƙashin Asusun Bunƙasa Noma na Ƙasa (NADF) ta ƙaddamar da kashi na farko na Shirin Tallafin Kayan Aikin Noma (FISP) a yankin Arewa maso Yamma, inda aka raba buhunan taki 100,800 ga ƙananan manoma 25,200 a jihohin Katsina, Kano, Kaduna, Kebbi da Jigawa. Da yake jawabi a wajen ƙaddamar da shirin a…
