Gwamnatin Tarayya Za Ta Kafa Cibiyoyin Kiwo a Yankuna Shida — Ƙaramin Ministan Noma

Gwamnatin Tarayya ta bayyana cewa ta yi shirin kafa cibiyoyin kiwon shanu a dukkan yankuna shida na ƙasar nan.

Ƙaramin Ministan Noma, Dakta Aliyu Sabi Abdullahi, shi ne ya bayyana hakan a rana ta biyu ta taron tattaunawa tsakanin gwamnati da ‘yan ƙasa, da kuma nazarin rabin wa’adin mulkin Tinubu.

Taron, wanda Gidauniyar Sa Ahmadu Bello ta shirya, yana gudana ne a Gidan Arewa, a Kaduna.

A cewar ministan: “Aikin haɗin gwiwa da haɗin kai tsakanin Ma’aikatun Noma, Muhalli, Albarkatun Ruwa, Bunƙasa Kiwon Dabbobi da kuma Tattalin Arzikin Ruwa yana da matuƙar muhimmanci domin cika manufofin Ajandar Sabunta Fata.”

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *