Muna gargadin duk wani ɗan Najeriya da ke taimaka wa ’yan ta’adda — Christopher Musa

Shugaban Rundunar Tsaron Najeriya (CDS), Laftanar Janar Christopher Musa, ya gargadi duk wani ɗan Najeriya da ke taimaka wa ’yan ta’adda, da cewa gwamnati za ta ɗauki mataki mai tsauri a kansu.

A cewarsa: “Masu taimaka wa ‘yan bindiga da rahotanni ko kayan aiki, ku sani, abokin barawo barawo ne. Don haka ba za mu bar ku ba.” Musa ya bayyana hakan ne a wajen taron Sir Ahmadu Bello Foundation da ya gudana a Arewa House a Kaduna.

Hakazalika, ya kuma ce akwai cikakken haɗin kai tsakanin Najeriya da makwabtan ƙasashe irin su Nijar da Benin wajen tabbatar da tsaro a yankin Sahel da Arewa. Ya bayyana cewa wannan haɗin gwiwa yana ƙara ƙarfafa matsayinsu wajen magance barazanar ta’addanci.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *